Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Yi wa Baki Rijista

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta kafa wani kwamitin ƙwararru da zai yi aikin yiwa baƙi ƴan ƙasashen waje mazauna birnin rijista musamman waɗanda suke gudanar da kasuwanci.

Gwamnati ta ce ta ɗauki matakin ne domin samun alƙaluman mutanen da suka fito daga ƙasashen ƙetare kuma suke gudanar da harkokin kasuwanci a jihar, ta yadda za a haɓɓaka kudin shiga da kuma tsaro da samar da ayyukan yi.

Kwamitin wanda ke ƙarƙashin ofishin sakataren gwamnatin Kano, zai tattara bayanan baƙi ƴan ƙasashen waje da ke aiki walau na kamfani ko a wata ma’aikata ko kuma kasuwanci.

Shugaban kwamitin, Lawan Isa Kibiya ya ce aikin da za su yi zai taimaka wajen tabbatar da ganin baƙin waɗanda mafi yawa ƴan kasuwa ne su na biyan haraji kamar yadda doka ta yi tanadi.

Talla

Ya ƙara da cewa hakan zai bai wa gwamnati ƙwarin gwiwar ‘‘ƙoƙarin ganin ta samar da yadda za ta ba su kariya ta fuskar tsaro’’

Kwamishinan ma’aikatar ciniki ta jihar Kano, Alhaji Adamu Aliyu Kibiya wanda manba ne a kwamtin ya ce ‘‘aikin bai taƙaita ga buƙatar tattara haraji kaɗai ba, duk duniya akwai ƙa’idoji da aka kafa a doka, waɗanda idan baƙo ya je zai yi kasuwanci ga ƙa’idojin da ya kamata ya bi, sannan su ma ƴan gari ga ƙa’idojin da ya kamata su bi.’’

Ya ƙara da cewa ‘‘idan ka shiga wannan manyan kasuwannin namu, musamman kantin kwari, za ka ga baƙin su ne mafi yawa ke ƙerawa, su yi packaging su kuma yi kasuwanci kai tsaye.’’

Zargin cin zarafi: Gwamnan Kano ya kafa kwamitin bincike a kan kwamishiniyar Jin kai

Adamu Kibiya, ya kara da cewa ire-iren waɗannan abubuwan gwamnati ta kalla shi yasa ake ƙoƙarin fito da tsarin da zai taimaki al’umma musamman wajen samar da ayyuka da kare martabar kasuwanci: ‘‘Idan muka zura ido mu ka yi gaba to zai zamo nan gaba mun koma maula, mutanen mu sun koma bara. Don haka gwmanati ta duba, ta ga dole wannan abubuwa a taka masu birki.’’

 

Ya ƙara da cewa tsarin zai tsaftace harkokin kasuwanci a jihar, musamman yadda aka saba samun masu yi wa ƴan kasuwa zambo domin kwashe masu kuɗi, kuma ana samun irin waɗannan bata gari masu aikata daga kowanne ɓangare.

‘‘Za ka ga ana karɓar kayansu da yawa ana cinyewa, kuma su ma daga cikin su ana samun masu cinye wa ƴan kasuwar Kano kaya ko kuɗinsu, to gwamnati ta ga cewa dole ta shiga tsakani domin a kawo kyakkyawan yanayi na kasuwanci’’

Kwamitin dai ya tabbatar da cewa rijistar ba ta shafi ƴan wasu jihohin da suke zaune a jihar Kano ba, sannan kwamitin ya kunshi jami’an tsaro na ƴan sanda da DSS da hukumar kula da shige da fice da ƴan kasuwa da kuma shugabannin kungiyar ƴan China masu kasuwanci a jihar Kano, inda ake fatan nan da makonni biyar kwamitin ya mikawa gwamnati rahotansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...