Cire Kwamishiniyar jin ba zai Haifawa gwamnatin Kano da mai Ido ba – Shugaban APC Integrity

Date:

Daga Abubakar Isa

 

Tsohon Babban mataimaki na musamman ga tsohon gwamnan jihar kano Alhaji Ado Yellow Mai Tv ya yi kira ga gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da ya bi a hankali ka da wasu marasa kishin Kano su zuga shi ya cire Kwamishiniyar jin kai Hajiya Amina HOD daga mukaminta.

” Mu yan jam’iyyar APC ne, amma mun gamsu da cewa kwamishiniyar ma’aikatar jin kai Hajiya Amina HOD aikinta ta gudanar a matsayinta ta wacce take kula da jin kan al’umma, don haka bai da ce don mutum yayi Aikinsa ba kuma wasu su zo su yi masa sharri kuma har a yarda da bayansu”.

Alhaji Ado Yellow Mai Tv ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da yayi a Kano.

Talla

Ado Yellow wanda shi ne shugaban kungiyar APC integrity group na jihar Kano ya ce bai dace a harkar da ta shafi kiwon lafiyar al’umma a sanya siyasa ba, shi yasa suka ga dacewar tsuma baki akan wannan batu, kasancewar jihar kano ita suke kallo ba wani abu ba.

” Kowa yasan yadda likitoci a Kano suka yi kaurin suna wajen cin zarafin marasa lafiya da sauran al’umma, don haka mu muna ganin ba gaskiya ba ne abun da likitar nan ta fada , saboda mun fahimci kawai so likitocin suke sai sun gamsar da mutane akan karya, to muna so ku sani Mun gano ku”. Inji Ado Yallow

Gwamnan Kano Ka Cire Kwamishiniyar Jin Kai Saboda Za ta Jawo Maka Bakin Jini -Anas Abba Dala

Ya ce kiran da Kungiyar likitocin ta yiwa gwamnan jihar kano na ya cire Kwamishiniyar raini ne, ita kungiyar ai bata Isa ta cewa gwamna ga abun da zai yi ba , sai dai ta kai masa koke shi kuma ya duba ya dauki matakin da ya dace.

” Ina kira ga mai girma gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da ya bincika ya kuma tabbatar da cewa bai cire Kwamishiniyar ba, saboda aikin da ya dora mata ta yi, kuma idan har wata kungiyar zata yi maka barazana kuma ka bi Abin da take so, to gaskiya za a sa kai ta rabuwa da mutanen kirki a gwamnatinka”. A cewar Ado Yellow mai Tv

Ya ce duk da cewa su yan jam’iyyar APC ne amma sun yarda da nagartar Hajiya Amina HOD, don haka ne ma suka ga dacewar shiga maganar, saboda idan aka ce an cireta daga wannan mukamin to jihar Kano ce zata cutu saboda jajirtacciya ce mai kishin al’umma.

Idan za’a iya tunawa dai kadaura24 ta rawaito cewa an sami rashin jituwa tsakanin kwamishiniyar ma’aikatar jin kai ta jihar kano Hajiya Amina HOD da wata likita a asibitin kwararru na Murtala Muhammad, wanda har ta kai ga kungiyar likitoci da wasu yan siyasa sun fara kira ga gwamnan Kano da ya sauketa daga mukamin kwamishiniya.

Hakan dai ya jawo har sai gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kafa wani kwamiti karkashin jagorancin kwamishinan lafiya na jihar kano domin su binciki lamari tare da gabatar masa da rahoton binciken cikin kwana biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...