Daga Maryam Muhammad Ibrahim
Tsohon shugaban Najeriya a zamanin mulkin Soja Janar Yakubu Gowon dake bikin cika shekaru 90 a duniya ranar asabar, ya ce ya sami labarin cewar za ayi masa juyin mulki daga hukumomin tsaronsa tun kafin ayi kuma sunayen mutanen da aka gabatar masa na manyan jami’ansa ne da suka fito daga jiharsa ta Benue-Filato ta wancan lokaci.
Gowon ya bayyana sunayen kwamandan dakarun dake tsaron fadar shugaban kasa da suka hadar da Joe Garba da Tony Ochefu, amma sai ya ki amincewa da rahotan ganin saboda sun fito ne daga jiharsa, kana kuma dukkansu Kiristoci ne.
Janar Gowon ya ce ya yi kokarin ji daga Ochefu amma bai iya kai wa gare shi ba, ya yin da shi kuma Joe Garba ya yi ta rantsuwar cewar babu wani abu mai kama da haka.
![](https://kadaura24.com/wp-content/uploads/2024/10/IMG-20240925-WA0001-300x225.jpg)
Tsohon shugaban ya bayyana mutanen 2 a matsayin masu kima a wurinsa saboda yadda suka taimaka masa wajen tabbatar da Najeriya ta kasance kasa guda.
Gowon ya ce a lokacin sai bukatar tafiya taron shugabannin kasashen Afirka ta taso, kuma shi ke matsawa takwarorinsa a kan su daina kauracewa taron, saboda haka ya tafi Kampala dake kasar Uganda tare da kwamishinan yan sanda Farouk Usman, kuma a wajen taron shugaban Uganda na lokacin Idi Amin ya shaida masa cewar an kifar da gwamnatinsa.
![](https://kadaura24.com/wp-content/uploads/2024/10/IMG-20241013-WA0026-211x300.jpg)
Yakubu Gawon dai ya mulki Nigeriya daga ranar 1 ga watan Ugusta na Shekarar 1966 zuwa ranar 29 ga watan juli na Shekarar 1975 Daily Trust