Rikicin NNPP: Kar ka saka ni a abun da bai kamata na shiga ba – Kwankwaso

Date:

Daga Sani Danbala Gwarzo

 

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce ya yanke shawarar kin cewa komai game da rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyar a jihar Kano.

Kwankwaso, da manema labarai suka tambaye shi a gidansa na Miller road da ke Kano da yammacin ranar Talata, ya ce ba shi da wani abin cewa a kan lamarin.

Talla

“Don Allah Bana son yin magana akan wannan batun . Kar ka sa ni cikin abin da bai kamata a na shiga ba. Shugaban jam’iyyar ya yi magana kuma yana magana, ku je gare shi,” Kwankwaso ya fadawa manema labarai.

Sabon Rikici: Jam’iyyar NNPP a Kano ta dare gida biyu

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren gwamnatin jihar Kano, Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da kwamishinan sufuri, Muhammad Diggol daga jam’iyyar.

A cewar Dungurawa, dakatarwar ta biyo bayan korafe-korafensu da ake kaiwa shugabannin mazabunisu da na kananan hukumomi na jam’iyyar.

Talla

Dungurawa ya ce an dakatar da su ne saboda rashin mutunta jam’iyyar da shugabancinta.

Idan za a iya tunawa a yan Kwanakin nan ana ta zargin Sakataren gwamnatin Kano Dr. Baffa Bichi bisa daukar nauyin wata kungiya mai suna ” Abba tsaya da kararka” wacce take rajin ganin an sami farraku tsakanin Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa Rabi’u Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...