Rikicin PDP: Gwamnonin PDP sun bayyana Matsayarsu

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnonin babbar jam’iyyar adawa a Najeriya ta PDP sun soke dakatarwar da aka yi wa muƙaddashin shugaban jam’iyyar na ƙasa, Iliya Damagum.

Gwamnonin sun kuma soke dakatarwar da aka yi wa sakataren hulɗa na ƙasa na jam’iyyar, Debo Ologunagba, da mai ba da shawara kan harkokin shari’a, Kamaldeen Ajibade.

Wannan na kunshe ne cikin jawabin da shugaban gwamnonin jam’iyyar kuma gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya yi wa manema labarai a safiyar yau Talata.

Bala ya ce Damagum ne shugaban jam’iyyar da suka sani yanzu kuma shi zai ci gaba da riƙe kujerar.

Tun da farko dai, wani ɓangaren kwamitin zartaswar jam’iyyar na ƙasa da ya ɓalle ya sanar da naɗa Yayari Mohammed a matsayin wanda zai maye gurbin Damagum, inda kowane ɓangare ya yi iƙirarin dakatar da ɗayan.

Talla

A wata sanarwa ranar Lahadi, Yayari ya ce kwamitin zartaswar jam’iyyar ya naɗa shi ne domin mayar da dawo da jam’iyyar kan turba.

Ya ce PDP ba ta yin adawa yadda ya kamata saboda kowa ya ɗora buƙatar kansa a gaba kafin ta jam’iyya – musamman ma wasu jagororin kwamitin na zartaswa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...