Sojojin Nijeriya sun sake hallaka kasurgumin dan fashin daji a Katsina

Date:

Dakarun Nijeriya sun sake samun nasarar hallaka kasurgumin dan fashin daji a Katsina.

A wata babbar nasara a yakin da ake yi da ta’ddanci, an kashe kasurgumin dan fashin dajin nan, Sani Wala Burki wanda ke addabar kananan hukumomin Safana da Batsari a jihar Katsina.

Kafar yada labarai mai kawo rahoton tsaro a Arewa, Zagazola Makama ce ta rawaito cewa jami’an tsaro da ‘yan banga na sa kai a jihar Katsina ne suka hallaka dan fashin dajin tare da mayakansa.

Sojojin Nigeria sun Kashe Ƙasurgumin Dan ta’adda da ya addabi Arewacin Nigeria

Lamarin ya faru ne a daren jiya a yayin ‘yan bindigar suka yi yunkurin kai hari ga mazauna garin Safana.

A martanin da suka mayar ‘yan bindigar da suka samu hadin kai da jami’an tsaro sun fuskanci ‘yan bindigar.

 

Acewar mazauna garin, an kashe Burki da mayakansa da dama a yayin fafatawar.

Dole yan Nigeria su dawo daga rakiyar siyasar ubangida wajen zaɓen shugabanni — Shekarau

Sani Wala Burki dai ya shahara wajen kai hare-hare a yankin.

Hakan na zuwa ne bayan sojojin Nijeriya sun kashe kasurgumin dan fashin daji, Kachalla Sububu a jihar Zamfara.

Majiya: Zagazola Makama mai sharhi kan lamuran tsaro a yankin yammancin Afrika.

Daily Nigerian

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...