Ambaliyar Ruwan Maiduguri: Mazauna garin sun fara koma gidajensu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mazauna garin Maiduguri da ruwa daga madatsar ruwa ta Alau ya raba da muhallansu sun fara komawa gidajensu yayin da ruwa ke raguwa a hankali.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa da yawa daga cikin wadanda ambaliyar ta shafa da suka kwana a waje sun ce duk da ruwan ya lafa, ba su iya tantance asarar da suka yi ba.

“Muna gaggawar mu koma gidajenmu don ganin abin da ya rage a gidajenmu, don dauke wasu daga cikin dukiyoyinmu da suka rage,” in ji Ali Bana na gundumar Gwange.

Asibitin Best Choice Ya Kaddamar Da Sabuwar Na’urar Jarirai Ta (Jaundice) Irinta Ta Farko A Arewacin Najeriya

Musa Abdullahi na unguwar Gomari, ya ce ya samu damar zuwa gidansa.

“Daga abun da na gani har yanzu gidana yana cike da ruwa. Don haka dole mu sake yin kwanaki a waje kafin mu koma ciki,” in ji Abdullahi.

A halin da ake ciki kuma, wani rahoton halin da ake ciki kan ambaliyar da ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya OCHA ya fitar, ya ce fiye da mutane 239,000 ne ambaliyar ta shafa.

Jerin sunayen yan takara 38 da NNPP ta tsayar a zaɓen shugabannin kananan hukumomin Kano

Ambaliyar ta tilastawa wasu daga cikin mutanen da abin ya shafa kaura zuwa sansanin ‘yan gudun hijira na Muna, wanda yake dauke da ‘yan gudun hijira sama da 50,000.

“Jami’an gwamnati sun rika kwashe al’umma daga Inda ruwan yafi hatsari zuwa wasu warare da ruwan bai kai ba,” in ji rahoton.

NAN ta ruwaito cewa ambaliyar ruwan ta shafi hanyoyin sadarwa, wutar lantarki da ruwan sha a mafi yawan sassan garin. (NAN)

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...