Karin kudin mai: Gwamnan Legos ya sassautawa ma’aikatan jihar

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnatin jihar Legas ta baiwa ma’aikatan jihar damar su rika gudanar da aiki daga gidan har na tsahon watanni uku sakamakon karin farashin man fetur da aka yi a Nigeria.

Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya amince da hakan a wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban ma’aikatan jihar Mista Bode Agoro a ranar Laraba.

Yan arewa ku yi mana aikin gafara, mun gaza kare ku – ACF

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ba da rahoton cewa, a ranar 28 ga Fabrairu, gwamnan ya ba da umarnin cewa ma’aikatan za su yi aiki daga gida na wasu kwanaki.

Wannan Sabon matakin da gwamnatin jihar Lagos ta dauka ya nuna cewa ta sake tsawaita tsarin nata don saukakawa ma’aikatan gwamnatin jihar.

Ya ba da umarnin cewa ma’aikatan da suke matakin Albashin na 01 zuwa 14 an ba su damar yin aiki daga gida na kwana biyu a cikin kowanne mako, yayin da su kuma waɗanda su ke matakin Albashin na 15 zuwa 17 aka ba su damar yin aiki daga gida na kwana ɗaya a cikin mako.

Kotu ta tusa keyar alƙalin bogi zuwa gidan yari a Kano

An yanke shawarar ne don rage tasirin cire tallafin man fetur ga ma’aikata.

Sanwo-Olu ya bayyana cewa tsarin zai saukakawa mafi yawa daga cikin ma’aikata, kuma tsarin dama ce ga dukkanin masu aiki a ma’aikatu da hukumomin gwamnatin jihar daban-daban.

NAN ta ruwaito cewa karin wa’adin ya fara aiki ne daga ranar 4 ga watan satumba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...