Alkalin alkalan Nigeria , Ariwoola ya yi ritaya

Date:

 

Babban mai shari’a na ƙasa na 22, Olukayode Ariwoola ya yi ritaya a matsayin Alkalan Alkalan Nijeriya bayan cika shekarun aiki na shekara 70.

Ariwoola, wanda aka haife shi a ranar 22 ga watan Agusta a 1954, ritayar tasa ta kawo karshen aikin da ya shafe shekaru yana yi a fannin shari’a.

A ranar 22 ga watan Nuwamba na 2011 ne aka nada mai shari’a Ariwoola a matsayin alkalin kotun koli , sannan ya sama babban mai shari’a na Nijeriya a 27 ga watan Yuni na 2022 bayan ajiye aikin da mai shari’a Tanko Muhammad yayi.

Tinubu ya yi wa Nigeria illar da za a dade ba a gyarata ba – Atiku Abubakar

A ranar 21 ga watan Satumba na 2022, majalisar dattawa ta tabbatar da shi a matsayin babban alkalin Nijeriya.

Anasa rai dai, Kudirat Kekere-Ekun ce za ta gaje shi bayan majalisar shari’a ta kasa NJC, ta bada shawarar nada ta a mukamin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...