Farashin kayan abinci na daf da karyewa a kasuwa — Kwastam

Date:

Hukumar Kwastam ta Najeriya, ta buƙaci masu zanga-zangar yunwa da su yi tsammanin samun ragin farashin kayayyakin abinci na ba da jimawa ba.

Kwanturola-Janar na hukumar, Bashir Adewale Adeniyi ne, ya bayyana hakan a hedikwatar tsaro da ke Abuja a ranar Talata.

Adeniyi, yana cikin shugabannin tsaro da suka halarci taron sirri wanda babban hafsan hafsoshin tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ya kira.

Atiku ya gargadi hafsoshin tsaron Nigeria kan harbin masu zanga-zanga

Daily trust ta ruwaito cewa a ranar 1 ga watan Agusta ne dubban ‘yan Najeriya suka gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar kan tsadar rayuwa.

“Shigowa da kaya daga waje yana ɗaukar lokaci. Don haka ɗaya daga cikin abubuwan da shugaban ƙasa ya yi na rage tasirin farashin shigo da kaya shi ne dakatar da harajin Kwastam da haraji kan kayan abinci da ake shigowa da su na wani lokaci.

Talla
Talla

“Mun yi imanin cewa idan aka aiwatar da hakan, zai taimaka wajen rage farashin kayayyakin abinci a kasuwanni. Hukumar Kwastam ta Najeriya ta himmatu wajen aiwatar da wannan manufa.”

Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron, shugaban hukumar ta Kwastam ya ce za a yi wa wasu kayan abinci da ake shigowa da su rangwame ba tare da karɓar harajin ba domin karya farashinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...