An sace tsohon Shugaban tashoshin Jiragen Ruwa a Kano

Date:

Rahotanni a jihar Kano na cewa ‘yan bindiga sun sace wani tsohon Janar-Manaja na hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa, NPA.

Bayanai sun nuna cewa an sace Bashir M Abdullahi daga gonarsa da ke kauyen Sitti na karamar hukumar Sumaila ranar Laraba da almuru.

BBC Hausa ta rawaito rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ba ta da labarin sace mutumin kawo yanzu.

Amma bayanai sun nuna cewa ‘yan bindigar sun rika fakon mutumin ne har suka kai ga sace shi.

Hakan na faruwa ne a yayin da rahotanni suke cewa wasu ‘yan bindigar da suka tsere daga jihohin Katsina da Zamfara da kuma Sokoto – wadanda suke fama da matsalolin tsaro – sun fara samun mafaka a wasu yankuna na jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...