An sace tsohon Shugaban tashoshin Jiragen Ruwa a Kano

Date:

Rahotanni a jihar Kano na cewa ‘yan bindiga sun sace wani tsohon Janar-Manaja na hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa, NPA.

Bayanai sun nuna cewa an sace Bashir M Abdullahi daga gonarsa da ke kauyen Sitti na karamar hukumar Sumaila ranar Laraba da almuru.

BBC Hausa ta rawaito rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ba ta da labarin sace mutumin kawo yanzu.

Amma bayanai sun nuna cewa ‘yan bindigar sun rika fakon mutumin ne har suka kai ga sace shi.

Hakan na faruwa ne a yayin da rahotanni suke cewa wasu ‘yan bindigar da suka tsere daga jihohin Katsina da Zamfara da kuma Sokoto – wadanda suke fama da matsalolin tsaro – sun fara samun mafaka a wasu yankuna na jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...