Tinubu bai da mu da halin da yan Nigeria suke ciki ba – PDP

Date:

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya (PDP) ta ce jawabin da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya gabatar a ranar Lahadi, game da zanga-zangar da ke gudana a faɗin ƙasar bai taɓo abubuwan da masu zanga-zangar ke kokawa a kai ba.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi, wadda ta samu sa hannun sakataren yaɗa labarun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba, PDP ta ce “jawabin na Tinubu ya nuna yadda ƙarara, Jama’iyyar APC da shugaba Tinubu ba su damu da halin ƙunci da al’ummar ƙasar ke fama da shi ba.”

Talla
Talla

Tinubu dai ya yi jawabin ne kwana huɗu bayan da wasu matasa a Najeriya suka hau kan tituna domin nuna fushi kan halin matsin tattalin arziƙi da al’ummar ƙasar ke fama da shi.

Dino Melaye ya kalubalanci jami’an tsaro Kan kisan masu zanga-zanga a Kano

A cikin jawabin da ya gabatar da safiyar Lahadi, Tinubu ya buƙaci al’ummar ƙasar su yi haƙuri su dakatar da zanga-zangar ganin cewa ta yi sanadiyyar rasa rayuka a wasu jihohin ƙasar.

Zanga-zangar wadda ta fara a ranar Alhamis ta rikiɗe zuwa rikici a wasu jihohin ƙasar, lamarin da ya kai ga asarar rayuka da dukiyar al’umma.

Sanarwar da PDP ta fitar ta ci gaba da cewa “Jam’iyyar ta yi takaicin yadda ya kasa bayyana ƙwararan matakan da ya kamata a ce gwamnati ta ɗauka domin kawo wa al’umma sauƙin matsin da suke ciki a ƙasar.

Dalilin da ya sa ba zan dawo da tallafin man fetur ba – Tinubu

“Shugaban ƙasa ya kasa yin bayani kan buƙatun al’umma na ɗaukara matakan da za su rage tsadar man fetur da magance faɗuwar darajar naira da kuma samar da abinci ga al’ummar da ke cikin yunwa,” in ji sanarwar.

Shi dai Tinubu a jawabin nasa na ranar Lahadi, ya ce gwamnatinsa ta ɗauki matakai kamar na shirin bai wa ɗalibai bashin karatu, da raba wa jihohi maƙudan kuɗaɗe da kuma bayar da tallafin abinci ta hannun gwamnoni.

Sai dai masharhanta da dama sun soki jawabin na Tinubu, inda suka ce ya gaza taɓo buƙatun masu zanga-zangar kai-tsaye.

Kuma tuni ƙungiyoyin da suke jagorantar zanga-zangar suka lashi takobin ci gaba da gudanar da ita a yau Litinin.

Ƙungiyoyin kare hakkin bil’adama dai sun zargi jami’an gwamnati da bude wuta kan masu zanga-zanga, kuma sun buƙaci hukumomi su yi bincike a kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...