Dino Melaye ya kalubalanci jami’an tsaro Kan kisan masu zanga-zanga a Kano

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Tsohon dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata a jihar Kogi, Sanata Dino Melaye, ya gargadi jami’an tsaro kan musgunawa masu zanga-zanga.

Akwai rahotannin da ke cewa wasu matasan Najeriya da ke zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya sun shiga hannun ‘yan sanda da wasu jami’an tsaro.

Talla
Talla

An yi zargin an harbe wasu masu zanga-zangar ranar Asabar a jihar Kano bayan zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa ta rikide zuwa tashin hankali.

Da yake magana kan lamarin, Dino Melaye a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X wato Twitter, ya bayyana rashin gamsuwa da yadda jami’an tsaro su ke cin zarafin masu zanga-zangar.

Rundunar yan sanda ta Kano ta yi karin haske kan abun da ya faru a unguwar kurna

Ya kuma bukaci jami’an da su daina cin zarafin masu zanga-zangar, domin tabarbarewar tattalin arzikin ya shafar kowa da kowa ciki har da su.

Sanarwar ta kara da cewa, “Kasuwa daya muke zuwa da ku, gidan mai daya, Naira daya muke kashewa, ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro ba su da wata kasuwa ta musamman ko gidan mai na musamman.

“Ku kula da mutane da girmama su, domin yan uwanku ne idan zaukin ya zo kuma za ku amfana, kuma dokar kasa ce ta basu damar yin hakan ”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...