Dino Melaye ya kalubalanci jami’an tsaro Kan kisan masu zanga-zanga a Kano

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Tsohon dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata a jihar Kogi, Sanata Dino Melaye, ya gargadi jami’an tsaro kan musgunawa masu zanga-zanga.

Akwai rahotannin da ke cewa wasu matasan Najeriya da ke zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya sun shiga hannun ‘yan sanda da wasu jami’an tsaro.

Talla
Talla

An yi zargin an harbe wasu masu zanga-zangar ranar Asabar a jihar Kano bayan zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa ta rikide zuwa tashin hankali.

Da yake magana kan lamarin, Dino Melaye a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X wato Twitter, ya bayyana rashin gamsuwa da yadda jami’an tsaro su ke cin zarafin masu zanga-zangar.

Rundunar yan sanda ta Kano ta yi karin haske kan abun da ya faru a unguwar kurna

Ya kuma bukaci jami’an da su daina cin zarafin masu zanga-zangar, domin tabarbarewar tattalin arzikin ya shafar kowa da kowa ciki har da su.

Sanarwar ta kara da cewa, “Kasuwa daya muke zuwa da ku, gidan mai daya, Naira daya muke kashewa, ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro ba su da wata kasuwa ta musamman ko gidan mai na musamman.

“Ku kula da mutane da girmama su, domin yan uwanku ne idan zaukin ya zo kuma za ku amfana, kuma dokar kasa ce ta basu damar yin hakan ”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...