Da dumi-dumi: Gwamnatin jihar Kano ta sassauta dokar hana fita

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da sassauta dokar hana fita ta sa’o’i 24 da ta sanya a jihar a jiya na tsawon sa’o’i 5.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa gwamnan jihar kano,Abba Kabir Yusuf ya sanya dokar hana fita a ranar Alhamis bayan zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa ta rikide zuwa tashin hankali wanda ya kai ga rasa rayuka da sace-sace.

Talla
Talla

Gwamnan ya ce an sassauta doka daga 12 na rana zuwa karfe 5 na yamma domin baiwa mutane damar zuwa sallah Juma’a.

Da yake magana a madadin gwamnatin Kano Kwamishinan Shari’a na jihar Barr. Haruna Isa Dederi gwamnati ba zata lamunci karya dokar da ta sanya ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...