Yadda masu zanga-zanga suka fara kone-kone a kofar gidan gwamnatin Kano

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Wasu daga cikin masu zanga-zangar nuna adawa da wahalhalun da ake fama da su a fadin Nigeria, sun fara kona tayoyi a kofar gidan gwamnatin jihar Kano a safiyar ranar Alhamis.

Masu zanga-zangar da su ka fito daga sassa daban-daban na birnin Kano sun yi dandazo ne a gidan gwamnati, inda gwamna Abba Kabir Yusuf zai yi musu jawabi.

Wasu daga cikin masu zanga-zangar ne suka hada tayoyi, kuma suka banka musu wuta a lokacin da suke tunkarar kofar.

Hakan ya sanya jami’an tsaron da ke gidan gwamnati suka harba bindiga sama da barkonan tsohuwa domin tarwatsa masu zanga-zangar.

Hakan tasa masu zanga-zangar suka rika guduwa zuwa wurare daban-daban .

Sai dai zuwa yanzu abubuwa sun daidaita domin jami’an tsaro su yi nasarar hana kona tayoyin , Inda suka bukaci masu zanga-zangar da su gudanar da zanga-zangar cikin lumana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...