Ana rige-rigen karbar Karin Zabe a Kano – Kwankwaso

Date:

 Gwamnatin jihar Kano ta ce ana samun karuwar masu rajistar zabe a jihar sakamakon fahimtar da al`umma ke yi game da muhimmancin zabe.

Gwamnatin jihar Kanon ta kafa wani kwamiti na musamman wanda ya shiga shelar wayar da kan al`umma, bayan ta gano cewa mutane da dama na dari-dari da yin rajistar zabe.

An kafa kwamitin wayar da kan masu zabe ne a jihar bayan rahotanni sun nuna cewa a jihohi da dama a Najeriya ciki har da Kanon, akwai tarin katunan zabe jibge a ofisoshin hukumar zabe, wadanda ke neman yin kwantai saboda masu katunan basu je sun karba ba.

Hakama akwai wadanda katunan su suka bata, ko suka lalace, da kuma wadanda suka cancanci kada kuri`a masu yawan gaske da basu je an yi musu rajistar ba.

BBC Hausa ta rawaito a cewar mataimakin shugaban kwamitin kuma kwamishinan raya karkara Alhaji Musa Iliyasu Kwankwaso, babban burin gwamnati dai shi ne kare matsayin jihar Kanon na rumbun kuri`a.

Ya kara da cewa ” abunda suke gani a zahiri na nuna cewa kwalliya na biyan kudin sabulu “.

A babban zaben 2019 jihar Kano ce tazo ta biyu wajen yawan masu kada kuri`a a fadin Najeriya da mutum sama da miliyan biyar, inda ta zo bayan jihar Legas mai mutum fiye da miliyan shida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...