Sarkin Gaya Ya Karbi Takardar Kama Aiki a Karo Na Biyu Daga Gwamnan Kano

Date:

Mai Martaba Sarkin Gaya Alhaji Aliyu Abdulkadir Gaya ya karbi takardar nadinsa na zama sabon Sarkin Gaya mai daraja ta biyu.

Sarkin dai shi ne daya tilo a cikin sarakuna biyar da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya mayar da shi.

Hakan ya biyo bayan amincewarsa ga sabuwar dokar da majalisar dokokin jihar Kano ta yi, wadda ta amince da kafa sarakunan Gaya, Rano, da Karaye guda uku masu daraja ta biyu.

Talla

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24, ta ce an dawo da Aliyu Ibrahim bisa cancanta da kuma jajircewarsa na yi wa al’ummar Masarautar Gaya hidima da suka hada da kananan hukumomin Gaya, Ajingi, da Albasu.

Da dumi-dumi: Shugaba Tinubu ya ayyana mafi ƙarancin albashi

“Za ku iya tunawa cewa Sarkin Gaya ne kadai ya karbi kaddara a lokacin da aka rushe masarautu biyar, aka sauke dukkan sarakunan.” Sanarwar ta kara da cewa.

Sarkin Gaya ya isa gidan gwamnatin Kano tare da rakiyar daukacin sarakuna da sauran masu rike da sarautar gargajiya na masarautar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...