Sarkin Gaya Ya Karbi Takardar Kama Aiki a Karo Na Biyu Daga Gwamnan Kano

Date:

Mai Martaba Sarkin Gaya Alhaji Aliyu Abdulkadir Gaya ya karbi takardar nadinsa na zama sabon Sarkin Gaya mai daraja ta biyu.

Sarkin dai shi ne daya tilo a cikin sarakuna biyar da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya mayar da shi.

Hakan ya biyo bayan amincewarsa ga sabuwar dokar da majalisar dokokin jihar Kano ta yi, wadda ta amince da kafa sarakunan Gaya, Rano, da Karaye guda uku masu daraja ta biyu.

Talla

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24, ta ce an dawo da Aliyu Ibrahim bisa cancanta da kuma jajircewarsa na yi wa al’ummar Masarautar Gaya hidima da suka hada da kananan hukumomin Gaya, Ajingi, da Albasu.

Da dumi-dumi: Shugaba Tinubu ya ayyana mafi ƙarancin albashi

“Za ku iya tunawa cewa Sarkin Gaya ne kadai ya karbi kaddara a lokacin da aka rushe masarautu biyar, aka sauke dukkan sarakunan.” Sanarwar ta kara da cewa.

Sarkin Gaya ya isa gidan gwamnatin Kano tare da rakiyar daukacin sarakuna da sauran masu rike da sarautar gargajiya na masarautar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...