Sabbin Sarakunan Rano da Karaye sun ziyarci Sarki Sanusi II

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Sabbin sarakunan Rano da Karaye da aka nada a matsayin masu daraja ta biyu sun yi mubaya’a ga Sarkin Kano na 16 Malam Muhammadu Sanusi II a ranar Laraba.

Sun kai wa sarki Sanusi II ziyarar ne sa’o’i kadan bayan Gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ya bayyana nadin nasu.

Sabbin sarakunan sun hada da: Alhaji Muhammad Maharaz na Karaye, Muhammad Isah Umar na Rano, da Alhaji Aliyu Abdulkadir na Gaya.

Talla

A wani faifan bidiyo da wakilin kadaura24 ya gani, sarakunan masu daraja ta biyu sun yi mubaya’a ga Sarki Sanusi a zaman fadar da aka gudanar a ranar Laraba.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya soki gwamnatin Kano kan sabbin masarautu masu daraja ta biyu

Duk sarakunan biyu sun yi alkawarin yin aiki a karkashin masarautar Kano mai daraja ta daya tare da gode wa Gwamna Abba Yusuf bisa ganin sun cancanta har ya nada su .

Idan za a iya tunawa, a ranar jiya talata 16 ga Yuli, 2024, Gwamnan ya rattaba hannu a kan dokar kafa masarautu masu daraja ta biyu a jihar. Masarautar Rano da ta kunshi kananan hukumomin Rano, Kibiya, da Bunkure; sai masarautar Gaya da ta kunshi kananan hukumomin Gaya, Ajingi, da Albasu; ita kuma Karaye ta kunshi kananan hukumomin Karaye da Rogo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...