Kofa ya shirya taron addu’o’i da gangamin motsa Jam’iyyar NNPP

Date:

Daga Zakaria Adam Jigirya

 

Ɗan Majalisa mai wakiltar mazaɓar kananan hukumomin Kiru/Bebeji a jihar Kano, Hon Abdulmumin Jibrin Kofa, a ranar Lahadi ya shirya taron addu’a na musamman a gidansa da ke Kofa, Bebeji, inda ɗaruruwan malamai suka yi wa mazabarsa da Kano da ma Najeriya addu’a.

Daga bisani kuma ɗan majalisar ya shirya babban taron motsa jam’iyya wanda dubban magoya baya suka halarta, inda ya jinjina musu kan jajircewarsu da goyon bayan da suke bayarwa.

Talla

Hon. Kofa ya ba su tabbacin cewa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen ci gaba da bayar da tallafin da kuma ayyukan raya ƙasa da yake yi daga yi daga aljihunsa da kuma na gwamnatin tarayya .

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa tsohon Sanatan Kano ta tsakiya mukami

Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai Shugaban jam’iyyar NNPP na Kano, Hashimu Sulaiman Dungurawa da ’Yan Majalisar jiha na mazabar Kiru (Abubakar Tasi’u Rabula) da na Babeji (Ali Mohammed Tiga), Shugaban Ma’aikatan Jihar Kano, Abdullahi Musa da kuma dattawa (Alhaji Jibrin Dan-Ako da Alhaji Dankaka Hussaini Bebeji) da

Sani Ibrahim Paki
Hadimin ɗan majalisar kan yaɗa labarai
14-07-2024

Ga hotunan yadda aka gudanar da taron:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...

RMK@69: Kwankwaso Jagora Ne Mai Hangen Nesa, Abba Kuma Na Kawo Ci Gaba a Kano – Bakwana

Wani jigo a kungiyar Kwankwasiyya, kuma tsohon mai ba...