Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa tsohon Sanatan Kano ta tsakiya mukami

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da nadin Sanata Bashir Garba Lado a matsayin mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin majalisar dattawa .

Mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya sanyawa hannu a ranar Asabar.

Talla

Shugaban ya bayyana Lado Mohammed a matsayin gogaggen dan siyasa kuma dan kasuwa daga jihar Kano.

Iftila’i: Gobara ta tashi a masarautar Kano

Muhammad Bashir Garba Lado tsohon Sanata ne da ya wakilci Kano ta tsakiya kuma tsohon Darakta-Janar na hukumar kula da yan gudun hijira ta kasa.

Yanzu-yanzu: Tinubu ya baiwa Baffa Babban Dan’agundi Mukami

Ngelale ya ce Shugaba Tinubu “yana tsammanin sabon mai ba shi shawara na musamman kan harkokin majalisar dattawa zai yi amfani da kwarewarsa wajen inganta alakar dake tsakanin bangaren zartarwa da majalisa dattawa.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An dakatar da Shugaba da Sakataren kungiyar APC X Eagle forum

Kwamitin zartarwa na kungiyar APC X Eagle forum ya...

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...