Kafin Zuwan Gwamna Abba Kabir Yan Fansho a Kano Suna cikin Mawuyacin Hali – Sarki Sanusi II

Date:

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa namijin kokarin da yake yi na magance matsalolin ƴan fansho a jihar da kuma kula da ilimin ‘ya’ya mata.

Sani Abba Yola, Darakta a Ma’aikatar Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Kano a cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano, ya ce Sarkin ya yi wannan yabon ne a lokacin da ya karbi bakuncin Kwamishinan Yada Labarai, Baba Halilu Dantiye da takwaransa na Kimiyya da Fasaha da Ƙere-ƙere, Alhaji Mohammed Tajo Othman a fadar Sarkin.

A cewarsa, Sarki Sanusi ya bayyana cewa gwamnati mai ci ta mai da hankali ga ƴan fansho da a baya aka jefa su cikin halin ƙaƙanikayi saboda rashin biyan su haƙƙoƙinsu.

Talla

Ya kuma jaddada cewa, “Bambancin kula da rashin kula, wani lokacin kamar bambancin rayuwa da mutuwa ne ga mai karbar fansho ko iyalansa, wasu daga cikinsu sun mutu, mu tuna cewa dukkanmu muna da alhakin Allah Ta’ala kan hakkin cika wajibcinmu ga wadanda suka yi wa jihar hidima tsawon shekaru 35.”

Dalilan da suka sa lauyoyin Sarki Aminu Ado Bayero su ka fice daga shari’ar dambarwar masarautar Kano

Sarkin ya yabawa Gwamna Yusuf bisa kashe naira biliyan shida wajen biyan kudin fansho da aka yi a baya-bayan nan ga ‘yan fansho da kuma karin sakin naira biliyan biyar da aka ware domin ci gaba da biyansu, lamarin da ya rage wa ma’aikatan da suka yi ritaya raɗaɗi.

“Biyan Naira biliyan 11 a cikin shekara daya hakika abin yabawa ne,” in ji Sarki Sanusi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...