Covid-19 : Gwamnatin jihar Kano ta bada Sabon umarni ga ma’aikatan gwamnati a Kano

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Suleman

Gwamnatin jihar Kano ta umarci dukkan ma’aikatan gwamnati da su ci gaba da aiki ba tare da bata lokaci ba.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka aikowa Kadaura24 a ranar Larabar Nan.

Ya ce Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ba da wannan umarnin ne yayin taron Majalisar Zartarwa na mako-mako da ake gudanarwa a Fadar Afirka, gidan Gwamnati, Kano.

Malam Garba ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan nasarorin da aka samu a yaki da cutar ta COVID-19 a cikin jihar a cikin watanni uku da suka gabata.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, Manyan sakatarorin da shugabannin sassa a Ma’aikatansu da hukumomi ana basu Umarnin dasu tabbatar da cewa an bin ka’idoji da dokokin gwamnati na COVID-19 a wuraren ayyukansu.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito An umarci Ma’aikata a Kano da su kasance a gida tun ranar 18 ga watan Janairu, sakamakon bullar cutar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...