Covid-19 : Gwamnatin jihar Kano ta bada Sabon umarni ga ma’aikatan gwamnati a Kano

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Suleman

Gwamnatin jihar Kano ta umarci dukkan ma’aikatan gwamnati da su ci gaba da aiki ba tare da bata lokaci ba.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka aikowa Kadaura24 a ranar Larabar Nan.

Ya ce Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ba da wannan umarnin ne yayin taron Majalisar Zartarwa na mako-mako da ake gudanarwa a Fadar Afirka, gidan Gwamnati, Kano.

Malam Garba ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan nasarorin da aka samu a yaki da cutar ta COVID-19 a cikin jihar a cikin watanni uku da suka gabata.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, Manyan sakatarorin da shugabannin sassa a Ma’aikatansu da hukumomi ana basu Umarnin dasu tabbatar da cewa an bin ka’idoji da dokokin gwamnati na COVID-19 a wuraren ayyukansu.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito An umarci Ma’aikata a Kano da su kasance a gida tun ranar 18 ga watan Janairu, sakamakon bullar cutar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...