Dalilin da Yasa Gwamnan Kano Zai Samar da Sabbin Ma’aikatu a Jihar

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Alhaji Jibrin Ismail Falgore ya tabbatar da bukatar Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf na samar da sabbin ma’aikatu a jihar.

Shugaban majalisar ya ce an sanar da shi ne ta hanyar wata wasika da gwamna Yusuf ya aikewa majalisar dokokin jihar, inda ya bayyana aniyar gwamnatinsa na kafa sabbin ma’aikatu a jihar.

Gwamnan Kano ya turawa majalisa sunan dan Kwankwaso da mutane 3 domin nada su Kwamishinoni

Rt. Hon. Falgore ya karanta wasikar a gaban ‘yan majalisar, inda ya ambato gwamnan ya bayyana cewa kafa ma’aikatun da ake son kafawa na daga cikin tsare-tsaren gwamnatinsa na inganta ayyuka a jihar.

Dr. Gumi ya bayyana abubunwan da suka tattauna da jami’an tsaron Nigeria

Ma’aikatun da aka gabatarwa majalisar domin kafawa sun hada da ma’aikatar harkokin jin kai da kawar da talauci da ma’aikatar Ma’adanai da sabbin makamashi sai kuma Ma’aikatar Tsaron cikin gida na ciki da aiyuka na Musamman.

A cewar gwamnan, sabbin ma’aikatun za su taka rawar gani wajen inganta harkokin zamantakewa da tattalin arziki da samar da shugabanci na gari tare da sanya jihar a kan wani tsari na ci gaba mai dorewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...