Zargin rashin biyan haraji: Gwamnati ta maka kamfanin Binance a kotu

Date:

Gwamnatin Najeriya ta shigar da ƙara kan kamfanin hada-hadar kuɗin kirifto na Binance gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja.

Hukumar tara haraji ta Najeriya, FIRS ce ta sanar da matakin, kamar yadda gidan Talabijin na Channels ya ruwaito.

Gwamnatin dai na tuhumar kamfanin na Binance da aikata laifuka huɗu da ke da alaƙa da ƙin biyan haraji.

Cikin waɗanda ake ƙarar akwai Tigran Gambaryan da Nadeem Anjarwalla, dukkansu manyan shugabannin Binance da yanzu haka ke tsare a hannun hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa arzikin Najeriya zagon ƙasa.

Da gaske ne an tsare shugabannin Binance a Najeriya?

Tuhume-tuhumen da ake yi wa Binance sun haɗa da zargin ƙin biyan harajin VAT kan kayayyakin more rayuwa da harajin da kamfanoni ke biya na kuɗin shigar da suke samu da ƙin biyan kuɗaɗen harajin da suka karɓa da kuma haɗa baki da abokanan hulɗarsu wajen kaucewa biyan haraji ta shafinta.

A cewar gidan Talabijin na Channels, gwamnatin Najeriya tana zargin Binance da ƙin yin rajista da hukumar FIRS saboda dalilai na haraji da kuma saɓawa dokokin biyan haraji a ƙasar.

Da dumi-dumi: Kotu Ta Bayyana Shuruddan Bada Belin Murja Kunya

Ɗaya daga cikin tuhumar da ake yi ta shafi gazawar Binance na karɓa da kuma biyan nau’ikan haraji ga gwamnati kamar yadda yake a sashe na 40 na dokar FIRS ta 2007 da aka yi wa gyaran fuska.

Gwamnatin Najeriya ta ce tana kan ƙudurinta na tabbatar da cewa kamfanonin kirifto suna mutunta dokokinta na haraji tare da magance almundahana a tsakanin irin kamfanonin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...

Mun gano yadda yan Bauchi ke mamaye dazukan Kano – Gwamnatin Kano

Daga Nazifi Dukawa     Gwamnatin jihar Kano ta ce ta gano...