Ganduje yace a shirye yake ya sanya hannu a dokar ‘yancin cin gashin kai ga bangaren shari’a

Date:

Daga Nura Abubakar
 Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya bayyana cewa, nan ba da jimawa ba zai rattaba hannu a kan kudirin dokar da zata baiwa bangaren shari’a yancin cin fashin Kai a jihar Kano ta shekarar 2021.
 Gwamna Ganduje ya bayyana haka ne yayin bikin makon Kungiyar Alkalai ta kasa (MAN) na shekarar 2021, wanda aka gudanar a Coronation Hall, dake Gidan Gwamnatin Kano.
 Ya bayyana cewa yana farin ciki da Wannan taron Saboda ya zo a dai-dai lokacin da gwamnatin jihar Kano ta shirya tsaf don karba da Sanya hannu a dokar cin gashin Kan bangaren Shari’a da zarar Majalisar Dokokin jihar kano ta Amince da ita.
 Ganduje ya ba da tabbacin cewa, da zarar majalisar dokokin jihar ta Amince da Kudirin, ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da shi tare da fara aiwatar da dokar ba tare da bata lokaci ba.
 Ya kara da cewa gwamnatin jihar Kano ta himmatu wajen tabbatar da ‘yancin cin gashin kai tare da tabbatar da aiwatar da cin gashin kai ga bangaren shari’a.
 Gwamna Ganduje ya yi alkawarin cewa, jihar ta umarci Ma’aikatar Kudi da ta saki kudade ga Ma’aikatar Shari’a don halartar Babban taron Kungiyar Lauyoyin Najeriya (NBA) ga Alkalan Majistare da Alkalan Kotun Shari’a da Kuma reshen Kungiyar na Jiha.
 Gwamnan ya bayyana cewa, jihar za ta saki jimlar Naira Miliyan Dubu Takwas (N800,000,000), don sayan motoci ga bangaren wanda Kuma Majalisar Zartarwar ta jihar Tuni ta Amince da a fitar da kudaden.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...