Kotu ta rushe Shugabanin rikon APC a kwara

Date:

Babbar kotu ta yanke hukuncin rushe shugabannin riko da gwamnan Kwara ya naɗa a kananan hukumomi 16 na jihar

Kotun tace babu dalilin da zai sa gwamna ya rushe zababbun ciyamomi, kuma ya maye gurbinsu da kantomomi.
Jam’iyyar adawa PDP ta bayyana jin daɗinta kan matakin kotun, inda tace wannan nasara ce ga mulkin demokaraɗiyya.
Kwara – Babbar kotun jihar Kwara ta rushe kwamitin rikon kwarya da gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya naɗa domin su jagoranci kananan hukumomi 16 dake jihar.
Premium times ta ruwaito cewa gwamna AbdulRazaq ya naɗa shugabannin riko a ƙananan hukumomin jihar bayan dakatar da zababbu.
Amma a ranar Jumu’a, Mai shari’a Hassan Gegele, na babbar kotun jihar dake zama a Ilorin, ya bayyana matakin da gwamnan ya ɗauka da, “cin mutuncin mulki.”
Gegele ya yi hukunci ne kan ƙarar da wata ƙungiyar al’umma ta shigar a gabansa, tana ƙalubalantar naɗa kwamitin riko da gwamnan jihar ya yi.
Shin gwamnatin Kwara ta amince da hukuncin?
Da yake martani kan hukuncin kotun, Antoni Janar kuma kwamishinan shari’a, Salman Jawondo yace gwamnati zata ɗaukaka ƙara kan hukuncin.
“Muna tabbatar da cewa shari’a kan wannan lamarin ba ta kare ba, domin zamu ɗaukaka ƙara zuwa kotun Allah ya isa.”

16 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...