NCC ta dauki mataki akan layukan wayoyin wasu mutane a Nigeria

Date:

 

Hukumar sadarwa ta Najeriya, NCC ta sake jaddata umarninta ga kamfanonin sadarwar na ƙasar da su rufe duka layukan wayar da ba a haɗa su da lambar katin ɗa ƙasa ta NIN ba.

 

Daraktan yaɗa labaran hukumar, Mista Reuben Mouka, ne ya bayyana umarnin a lokacin wani taron kasuwanci da aka gudanar a Kaduna.

Rage ma’aikatu: Akwai yiwuwar ma’aikata su rasa aikinsu? Tinubu ya Magantu

Mista Mouka ya ce dole ne masu amfani da layin waya su haɗa shi da lambar katin ɗan ƙasarsu ta NIN.

Ya ce an ɗauki matakin ne don magance matsalar tsaron da ƙasar ke fuskanta.

Mista Mouka ya jaddada wa’adin yau Laraba, 28 ga watan Fabrairu da aka bai wa kamfanonin sadarwar su rufe duka layukan da ba a haɗa da lambar NIN ba.

Dama dai hukumar NCC ta ɗaɗe tana kiran al’ummar ƙasar da su haɗa lambar wayarsu da ta katin ɗan ƙasarsu wato NIN, a wani mataki na daƙile ayyukan matsalar tsaro a ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...