Daga Nura Abubakar
Shugaban Majalisar Limaman juma’a ta jihar Kano Kuma babban Limaman masallacin Juma’a na Sheikh Ahmadu Tijjani dake Kofar mata Sheikh Nasir Adam ya bayyana Cewa baya goyon bayan cakuduwar da ake yi tsakanin Maza da Mata a wuraren Maulidi.
Sheikh Nasir Adam ya bayyana hakan ne wajen Maulidin da Zawiyyar Marigayi Uba Ibrahim Ringim dake unguwar sabuwar kofa a birnin Kano.
Shehun Malamin yace ya Zama wajibi Malamai su Rika kula sosai wajen tabbatar da Mata basu hadu da Mata ba,Inda yace sau tari anfi Samun irin Wannan mummunar Dabi’ar Yayin da Dalibai suke zagayen kewaye Gari a Wannan Wata na Maulidi.
” Wannan mummunar Dabi’ar gaskiya tana neman Kara yawa a Cikin al’ummar mu ,Kuma hakan ba karamin kuskure bane Wanda hakan kan baiwa shedan da shedanun Mutane damar aiwatar da wancan shedanci a warwaren wancan zagaye.”
Sheikh Nasir Adam ya bukaci Iyayen yara da malaman makarantu dasu tashi tsaye wajen yakar Wannan mummunar Dabi’ar wadda take Kara Shigar al’ummar mu.
Delta airlines phone number https://about.me/DeltaAirlinesResedreservations