Na Warke sosai, yanzu Babu abun da yake damu na-Bola Tinubu

Date:

Jagoran jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, Asiwaju Bola Tinubu, ya dawo ƙasar nan bayan ya shafe wata kusan huɗu a birnin Landan sakamakon jinya.

Cikin wata sanarwa daga ofishin yaɗa labaransa a ranar Juma’a, Tinubu ya ce ya warke sarai tare da musanta “jitar-jitar da ake yaɗawa” kan rashin lafiyar tasa.

Ta ƙara da cewa an yi masa tiyata ne a gwiwarsa ta dama da kuma ba shi kulawar bayan tiyata.

“Mai girma Asiwaju Bola Tinubu ya sauka ne ranar Juma’a 8 ga watan Oktoba da yamma daga Landan,” a cewar sanarwar.

“Saɓanin abin da ake yaɗawa, ba a yi masa wata tiyata ba saɓanin wannan sannan kuma babu shirin yi masa wata nan gaba. Ya warke a kan lokaci kuma ba tare da wata matsala ba.”

Cikin sanarwar, Tinubu ya gode wa Shugaba Muhammadu Buhari “saboda ziyartarsa da ya yi a Landan” da gwamnoni da ‘yan majalisar yankin Arewa da ‘yan majalisar Jihar Legas.

An sha alaƙanta Bola Tinubu da neman takarar shugaban ƙasa a Najeriya, sai dai har yanzu dattijon mai shekara 69 kuma tsohon gwamnan Legas bai bayyana sha’awarsa ba ƙarara.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...