Bana goyon bayan cakuduwa tsakanin Maza da Mata a wajen Maulidi – Sheikh Nasir Adam

Date:

Daga Nura Abubakar

Shugaban Majalisar Limaman juma’a ta jihar Kano Kuma babban Limaman masallacin Juma’a na Sheikh Ahmadu Tijjani dake Kofar mata Sheikh Nasir Adam ya bayyana Cewa baya goyon bayan cakuduwar da ake yi tsakanin Maza da Mata a wuraren Maulidi.
Sheikh Nasir Adam ya bayyana hakan ne wajen Maulidin da Zawiyyar Marigayi Uba Ibrahim Ringim dake unguwar sabuwar kofa a birnin Kano.
Shehun Malamin yace ya Zama wajibi Malamai su Rika kula sosai wajen tabbatar da Mata basu hadu da Mata ba,Inda yace sau tari anfi Samun irin Wannan mummunar Dabi’ar Yayin da Dalibai suke zagayen kewaye Gari a Wannan Wata na Maulidi.
” Wannan mummunar Dabi’ar gaskiya tana neman Kara yawa a Cikin al’ummar mu ,Kuma hakan ba karamin kuskure bane Wanda hakan kan baiwa shedan da shedanun Mutane damar aiwatar da wancan shedanci a warwaren wancan zagaye.”
Sheikh Nasir Adam ya bukaci Iyayen yara da malaman makarantu dasu tashi tsaye wajen yakar Wannan mummunar Dabi’ar wadda take Kara Shigar al’ummar mu.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...