Za Mu Fara Daukar Mataki Akan Masu Yin Gine-Gine ba Tare da Neman Iziniba a Kano – KNUPDA

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da kwamitocin kar-ta-kwana don kula da haramtattun gine-gine, da kuma gine-gine da aka yi su ba tare da izini ba tare da kwacesu.

Manajan Darakta na Hukumar Tsara Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Arch. Ibrahim Yakub Adamu ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da jami’ar hulda da Jama’a ta ma’aikatar Bahijja Malam Kabara ta aikowa kadaura24.

Zanga-Zangar NLC: Kungiyar Yarbawa Ta Baiwa Yan Kabilar Umarni

Manajan daraktan ya bayyana dalilan kaddamar da kwamitocin da suka yi daidai da kishin Gwamnati mai ci na ganin Kano ta zama ta daya a tarayyar Nigeria a fannin tsara burane.

Ya nuna rashin jin dadinsa kan yadda ake ci gaba da yin gine-gine da kuma sayar da su ba tare da amincewar KNUPDA ba, yana mai gargadin cewa gwamnatin yanzu ta Alhaji Abba Kabir Yusuf za ta dauki matakan da suka dace a kan masu karya dokokin gwamnati.

Junaid Abdullah ne zai ya jagoranci kwamitin yayin da membobin suka haɗa da duk daraktoci da wakilan kamfanoni masu zaman kansu dake samar da rukunin unguwanni a Kano.

Marubucin Fim din Labarina Ya yiwa yan kallo Martani game da Shirin na Wannan makon jiya

A nasa bangaren Tpl Junaid Abdullahi ya bayyana cewa a shirye su ke su yi aiki tukuru domin cimma burin da ake so.

Shugaban ya kuma bukaci jama’a da su rika tuntubar masu unguwanni da hakimai da sauran masu ruwa da tsaki kafin su sayi duk wani fili.

Yankunan da suka ziyarta sun hada da Yankatsari a karamar hukumar Dawakin Kudu, Kumbotso, Gezawa da Nassarawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...