Tattalin arziki: Tinubu Ya Gana da Gwamnoni

Date:

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gana da gwamnonin ƙasar a zauren majalisar dokoki da ke Abuja.

Taron wanda aka fara da misalin karfe 11:30 na safe, ya samu halartar mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima da ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike; da Sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun.

Yadda Yan Majalisa ke Kokarin Mayar da Nigeria Tsarin Firaminista

Taron dai bai rasa nasaba da damuwar da ake nunawa a fadin kasar dangane da tsadar kayan abinci da rashin tsaro da sauran batutuwan da suka shafi tattalin arziki.

Taron dai ya biyo bayan taron Majalisar Tattalin Arzikin Kasa (NEC) na wata-wata, wanda mataimakin shugaban kasa Shettima ya jagoranta.

Aminu Dantata ya Bayyana Ra’ayinsa Kan Batun Sauya Tsarin Shugabanci a Nigeria

Bayan koke-koke da al’ummar kasar suka yi kan tabarbarewar tsaro da tabarbarewar tattalin arziki, shugaban kasar ya umarci ma’aikatar noma da samar da abinci ta saki kimanin tan dubu arba’in da biyu na masara da gero da sauran kayayyakin masarufi a cikin tsare-tsare don magance hauhawar farashin kayan abinci a kasar.

Shugaban ya kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da zuba ido kan ƙalubalen tattalin arziƙi da tsaro da Najeriya ke fuskanta.

Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu ta yi ciki har da cire tallafin man fetur ya zama dole, inda ta kara da cewa wadannan matakan za su haifar da riba nan ba da jimawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar almajirai da yaran da ba sa zuwa Makaranta ta kaddamar da yi wa yaran da ba sa zuwa Makaranta Rijista a Kano

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Hukumar kula da almajirai da yaran...

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Barau Jibrin

Daga Isa Ahmad Getso Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata...

Inganta tsaro: Shugaban K/H Tarauni ya ba da fili domin gina ofishin Civil Defence a karkasara

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Shugaban karamar hukumar Tarauni, Alhaji Ahmed...

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nada Malam...