Tsohon Gwamnan Kaduna Ya Koma Jam’iyyar APC

Date:

 

Tsohon gwamnan jihar Kaduna Mukhtar Ramalan Yero ya koma jam’iyyar APC, watanni kaɗan bayan ficewarsa daga jam’iyyar PDP.

Ramalan Yero ya sanar da ficewar tasa ne a wani bayani da ya yi wa manema labaru, yau Litinin a garin Kaduna.

Sarkin Kano ya Baiwa Matar Tinubu Sako Zuwa ga Shugaban Kasa

A bayanin nasa, tsohon gwamnan na jihar Kaduna ya ce ya koma APC ne bisa dalilai na ƙashin kansa bayan ya tattauna da waɗanda ke kusa da shi a harkar siyasa.

 

A cikin watan Oktoban shekarar 2023 ne Yero ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar PDP.

Tsadar Rayuwa A Najeriya Ba Laifin Tinubu bane, Ina da Dalili –Khalifa Sanusi II

Ramalan Yero ya riƙe gwamnan jihar Kaduna ne ƙarƙashin jam’iyyar PDP daga shekara ta 2012 zuwa 2015 bayan rasuwar tsohon gwamnan jihar Patrick Yakowa a wani hatsarin jirgin helikwafta.

Daga nan ne ya yi takarar gwamnan jihar a ƙarƙashin inwar jam’iyyar ta PDP sai dai bai yi nasara ba,

Daga baya Ramalam Yero ya sha yunƙurin sake yin takarar gwamnan jihar, sai dai bai samu nasarar hakan ba, inda ya gaza yin nasara tun a matakin zaɓen fitar da ɗan takara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...