Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya ta Magantu Kan yunkurin Kungiyar Kwadago

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin Najeriya ta ce ba abu ne mai yiwuwa ba a zartar da wasu daga cikin bukatun kungiyar kwadago da aka cimma a watan Oktoban 2023, da gaggawa ba.

Karamar ministar kwadagon kasar, Nkeiruka Onyejeocha ce ta shaida wa ‘yan jaridu a yau Juma’a yayin amsa tambayoyi ga ‘yan jaridun.

Tinubu Ya Bayar da Sabon Umarni ga Yan Nigeria

Gwamnatin ta tarayya ta kara da cewa daya daga cikin yarjeniyoyin wadda take neman a samar da cibiyoyin sauya motoci zuwa masu amfani da iskar gas zai dauki lokaci kafin cibiyoyin su wadata ko’ina kuma kwamitin da ke kula da samar da cibiyoyin yana aiki tukuru.

A watan Oktoban bara ne dai bangarorin biyu suka cimma jerin yarjejeniyoyi da suka kunshi ragewa ‘yan kasar radadin talauci sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnati ta yi.

Kungiyar Masu Makarantu Masu Zaman ta Janye Karar da Take Gwamnatin Kano Kotu

Sauran bukatun sun hada da samar da mafita ga darajar naira da tashin farashi da kuma matsalar tsaro da dai sauransu.

Kungiyar kwadago dai ta bai wa gwamnati wa’adin mako biyu da ta zartar da yarjeniyoyin ko ta tsunduma yajin aikin sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...