Dole Matasan Nigeria Su Nemi Ilimin Addini Dana Sana’a Don Dogaro da Kai – Barr. Dan almajiri

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Wani malamin addinin musulunci anan kano sheik Barrister Habib muhammad dan almajir fagge, yace dole sai matasa sun tsage damtse wajan neman ilimin addinin musulunci da kuma karatun sana’a, wanda zai basu damar dogaro da kawunansu Wanda hakan zai taimaka masu wajan kasancewa mutane na gari.

” Matasa sune kashin bayan cigaban al’umma don haka ya zama wajibi idan ana bukatar samun al’umma ta gari kowanne matashi ya zamana yana da Sana’ar yi da kuma ilimin addini”.

Jinkirin biyan albashi: Ma’aikatan gwamnati sun kalubalanci Tinubu

Sheikh Dan almajir ya bayyana hakane a bikin saukar karatun Littafin muwada na imamu malik da ya kwashe shekaru goma sha uku ana yana koyarwa a farafajiyar makarantar dake masalallacin juma’a na Daiba dake unguwar
Rinjyar lemo.

A yayin taron sheikh imam Barrister Habib dan almajir ya bayyana farin cikinsa game da yadda daliban suke bada goyan baya wajan halartar karatuttukan da ake gabatarwa ba tare da nuna gazawa ba.

Hukumar Yaki da Cin Hanci ta Kano ta Bayyana Yadda Zata Yaki Yan Kasuwa Masu Boye Kayan Masarufi

Yace baiwa dalibai ingantaccen ilimi da tarbiyya shi ne babban jigo na samun nasara a cikin rayuwarsu a duniya da lahira.

Taron ya samu halartar al’umma da dama wadanda suka hadarda khalifa Ahmad muhammad Dan almajir Alhaji Ali Abdurrahman da Alhaji Aminu sadauki

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...