Jinkirin biyan albashi: Ma’aikatan gwamnati sun kalubalanci Tinubu

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Wasu ma’aikatan gwamnati sun zargi gwamnatin shugaba Bola Tinubu da rashin kula da halin da ma’aikata ke ciki.

Ma’aikatan ta hanyar kungiyoyinsu sun yi wannan zargin ne kan jinkirin da ake samu na biyan albashi, tagomashi da sauran kudaden alawus-alawus.

Tsadar Kayan Abinchi: Kotu Ta Baiwa Gwamnatin tarayya Umarni

Kungiyar manyan ma’aikatan gwamnati ta ƙasa, ASCSN, ta bayyana rashin jin dadin ta musamman kan jinkirin biyan albashin ma’aikata na wata-wata.

Da yake magana da Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, Tommy-Etim Okon, Shugaban ASCSN ya ce ya kamata gwamnati ta gaggauta biyan albashi da alawus din ma’aikata.

Gobara ta Kone Kayan Abinchi da Dabbobi a Kano

Ya ce, tun lokacin da Shugaba Tinubu ya hau karagar mulki, ba a biyan albashin ma’aikata a kowane wata a kan lokaci, wanda hakan ke shafar samar da ayyukan yi da walwala.

A cewarsa, ya kamata gwamnati ta kula da halin da ma’aikata ke ciki, duba da irin halin kuncin da ake ciki a kasar nan.

“Kowace rana tsadar rayuwa tana kara hauhawa, ta yaya ma’aikata za su biya kudin mota zuwa ofis, ta yaya tattalin arziki da sauran masana’antu za su tsira, idan ba a samun hada-hadar kudade?

“Yau ne 8 ga Fabrairu, kuma zan iya gaya muku sarai cewa har yanzu ma’aikata da yawa ba su karbi albashinsu na watan janairu ba,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...