Tsadar Kayan Abinchi: Kotu Ta Baiwa Gwamnatin tarayya Umarni

Date:

Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta umarci Gwamnatin Tarayya da kayyade farashin kayan masarufi da na man fetur cikin kwanaki bakwai.

Mai shari’a Ambrose Lewis-Allagoa ya ba da wannan umarni ne ranar Laraba a shari’ar da mai rajin kare hakkin bil’adama Femi Falana ya maka Jukumar Kula da Farashin Kayayyaki da kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kan tsadar rayuwa a kasar.

Ban ce Na fi Yan Najeriya Shan Wahalar Tsadar Rayuwa ba, amma ina Fatan Matsalar ta zamo Tarihi -Dangote

Alkalin ya ba wa gwamnati kwana bakwai ta kayyade farashin madara, fulawa, gishiri, sukari, kekuna, ashana, babura da motoci da kayayyakinsu da kuma man man fetur da dizal da kananzir.

Falana ya garzaya kotun ne yana neman ta umarci hukumar kayyade farashi ta gudanar da aikinta, kamar yada dokar dokar kayyade farashin kaya ta tanadar.

Da dumi-dumi: An kai Batun Rushe Masarautun Kano da Mayar da Sanusi Matsayin Sarkin Kano Gaban Majalisa

Da yake mayar da martani, Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN), ta bakin mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Kamarudeen Ogundele, ya ce, “Da zarar mun samu kwafin hukuncin, za mu yi nazari a kai.

“Za mu dauki matakin da zai dace da kasar kuma mana tabbatar muku cewa wannan gwamnati za ta kasance da muradin talakawa a koyaushe,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...