Tsadar Kayan Abinchi: Tinubu na Ganawa da Masu Ruwa da Tsaki

Date:

A halin yanzu dai kwamitin shugaban kasa kan bada agajin gaggawa a sha’anin Abinchi na gudanar da taro a fadar shugaban kasa dake Abuja kan tsadar rayuwa a Nigeria.

Femi Gbajabiamila, shugaban ma’aikata fadar shugaban kasa ne ya kira kwamitin din, wanda shugaban kasa Bola Tinubu zai jagoranci.

Yunwa: Rarara ya raba kyautar kayan Abinchi da kuɗin cefane ga magidanta

Nuhu Ribadu, mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA); Yemi Cardoso, gwamnan babban bankin Najeriya (CBN); Tahir Mamman, ministan ilimi; Wale Edun; Ministan kudi da Abubakar Kyari, ministan noma, da Mustapha Shehuri da sauransu ne suka halarci tattaunawar.

Iftila’i: Gobara ta Hallaka Wani Yaro Dan Shekara 4 a Kano

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito mawuyacin halin da al’ummar Nigeria suke ciki sakamakon tabarbarewar tattalin arzikin kasar, wanda ya janyo tsadar rayuwa.

Hakan ne dai ta haddasa Zanga-Zangar lumana a jihar Neja, inda daruruwan mutane suka fito domin nuna damuwarsu kan halin da suke ciki na tsadar kayan Abinchi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...