Iftila’i: Gobara ta Hallaka Wani Yaro Dan Shekara 4 a Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wani yaro mai kimanin shekaru hudu mai suna Abubakar Sani sakamakon gobarar da ta tashi a Yakasai Layin Inuwa mai mai karamar hukumar birnin kano .

Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Alhaji Saminu Abdullahi ya bayyana hakan a Kano.

Saminu ya bayyana cewa, hukumar ta samu kiran gaggawa daga ma’aikacinsu Habibi Adamu game da barkewar gobara a Yakasai.

Ali Nuhu Ya Ziyarci Sarkin Kano, A Karon Farko

Ya kuma yi nuni da cewa, nan take aka hada tawagar ceto daga Ofishin hukumar kashe gobara dake Sakatariyar Audu Bako a birnin Kano .

Jami’in hulda da jama’a ya yi nuni da cewa, ginin bene daya mai tsawon mita 40 da 30 da ake amfani da shi a matsayin gidan zama, daki daya dake benen ne ya kone gaba daya sakamakon gobarar, yayin da falo daya ya dan kone.

Da dumi-dumi: Shugaban Karamar Hukuma a Kano Ya Ajiye Aikinsa

Ya ce, Yaron ya makale a dakin da wuta ta kama har ta cinye shi kuma duk kokarin da aka yi na ceto shi kafin isowar ‘yan kwana-kwana ya ci tura.

Saminu ya ci gaba da cewa, an ceto wanda abin ya shafa a sume kuma aka kai shi asibitin kwararru na Murtala Muhammed, inda likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da rasuwarsa.

Jami’in hulda da jama’a ya bayyana cewa, an mika mamacin ga mahaifinsa, Sani Hussaini domin yi masa jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Ya ce gobarar ta tashi ne sakamakon yadda yaron da abin ya shafa ke wasa da ashana a cikin daki.

Saminu ya bukaci iyaye da su daina jefa ’ya’yansu cikin hadari ta hanyar barin su ba tare da kula da su ba da kuma nisantasu da abubuwa masu hadari .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...