Daga Aliyu Danbala Gwarzo
Shugaban Karamar hukumar Nasarawa Auwal Lawan Shu’aibu wanda aka fi sani da aranposu ya bayyana ficewar sa daga jam’iyyar APC zuwa NNPP mai mulkin jihar Kano.
“Ungulu ta Koma gidanta na Tsamiya…….. Kuma fa His Excellency “ABBA KABIR” Masoyin talakawa ne da Kano, mucigaba da tayashi da adu’a” . A cewar Aranposu
Da dumi-dumi: Shugaban Karamar Hukuma a Kano Ya Ajiye Aikinsa
Auwal Lawan ya bayyana hakan ne a sahihin shafinsa na Facebook a safiyar talatar nan.
Tun da sanyin safiyar wannan rane dai aka wayi gari da wasu hutunan shugaban karamar hukumar ta Nasarawa da gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf yayin wata ziyara da ya kai masa.
Ali Nuhu Ya Ziyarci Sarkin Kano, A Karon Farko
A hotunan an ga Aranposu sanye da jar hula Wanda hakan Ke nuni da cewa ya koma tafiyar Kwankwasiyya da ya bari tun lokacin da aka raba gari tsakanin Kwankwaso da Ganduje.
Dama dai Aranposu yayi kaurin suna wajen sukar dan takarar gwamnan jihar kano a jam’iyyar APC duk da sun fito a karamar hukuma guda.
Kwanaki kadan ne dai suka ragewa shugabannin kananan hukumomi a jihar Kano.