Dole ne mu bi kadin abinda aka yi wa Jami’anmu – KAROTA

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Hukumar Kula da Zirga zirgar Ababen Hawa ta jiha KAROTA ta kama daya daga cikin wadanda ake zargi da farwa Jami’anta.

Hukumar ta sami nasarar kama matashin mai suna Saifullahi Haruna jim kadan bayan da wasu ɓata gari suka farwa Jami’an Hukumar wadanda suke bincike ababen hawa a kan titin Panshekara cikin burnin Kano.

Kotu ta sanya ranar saurarar karar da aka shigar don kalubalantar hukuncin da aka yanke wa Abduljabbar

Wasu ɓata garin matasa ne suka farwa Jami’an na KAROTA da misalin karfe 3 na dare a kan titin Panshekara cikin burnin Kano. Hukumar ta ce ba za ta zuba ido ta kyale ana cin zarafin Jami’anta ba, domin kuwa aiki suke bisa tsarin doka.

Kadaura24 ta rawaito Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da Jama’a na hukumar Nabulusi Abubakar ya sanyawa hannu.

Tuni dai Hukumar ta miķa wanda ta kama wajen Baturen Yansandan yankin da abin ya faru, domin fadada bincike tare da daukar matakin kama ragowar domin gurfanar da su gaban Shari’a.

Rundunar Yan sandan Kano Ta Kama Wani Kasurgumin Mai Garkuwa da Mutane

Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ya ce ya zama wajibi Hukumar ta mika godiyarta ga al’umma musamman waðanda suke ankarar da ita wani gyara idan buķatar hakan ta taso

Ya ce ķofar Hukumar a buðe take ga duk wanda yaga wani gyara ko shawara ya sanar da Helkwatar Hukumar ta KAROTA ko ya same mu a kan Lambar Waya 08023608861 domin ciyar da aikin Hukumar da jihar Kano ta ɓangaren Sufuri gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...