Tsadar Kayan Abinchi: Zanga-Zanga Ta Barke A Jihar Neja

Date:

Dandazon mutane sun mamaye Minna, Babban Birnin Jihar Neja, don nuna bacin ransu kan yadda kayan abinci ke ci gaba da tashin gwauron zabo.

Tun misalin karfe 7 na safiyar ranar Litinin, dandazon mutane suka yi tsinke suka tare hanyar Minna zuwa Bida, don nuna bacin ransu kan tsadar kayan abinci.

Hakan ya kawo tsaikon zirga-zirgar ababen hawa a birnin.

Soja ya bude wuta, ya kashe ogansa, ya raunata wasu a Sokoto

Jami’an ’yan sanda kawo dauki domin tabbatar da tsaro, amma wasu masu zanga-zangar suka yi kokarin kawo musu farmaki, lamarin da ya kai ga tarwatsa su da harbin bindiga.

Daya daga cikin masu zanga-zangar, Ibrahim Gana, ya koka kan yadda ake sayar da kwanon shinkafa Naira 2,000 a kasuwanni, yayin da masara ta kai Naira 1,000.

INEC ta Bayyana Sakamakon Yan Majalisun Jihar Kano Guda biyu

“Ya kamata Gwamnatin Tarayya ta dauki matakin rage wahalhalun da talakawan Najeriya ke sha, mutane ba za su iya jurewa ba.”

Kakakin rundunar, DSP Wasiu Abiodun, bai amsa kiran waya don yin karin haske kan lamarin ba.

Kayan masarufi na ci gaba da yin tashin gwauron zabo a Najeriya, lamarin da ya sanya talakawa yin kira ga shugabanni su kawo musu dauki.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...