Tsadar Kayan Abinchi: Zanga-Zanga Ta Barke A Jihar Neja

Date:

Dandazon mutane sun mamaye Minna, Babban Birnin Jihar Neja, don nuna bacin ransu kan yadda kayan abinci ke ci gaba da tashin gwauron zabo.

Tun misalin karfe 7 na safiyar ranar Litinin, dandazon mutane suka yi tsinke suka tare hanyar Minna zuwa Bida, don nuna bacin ransu kan tsadar kayan abinci.

Hakan ya kawo tsaikon zirga-zirgar ababen hawa a birnin.

Soja ya bude wuta, ya kashe ogansa, ya raunata wasu a Sokoto

Jami’an ’yan sanda kawo dauki domin tabbatar da tsaro, amma wasu masu zanga-zangar suka yi kokarin kawo musu farmaki, lamarin da ya kai ga tarwatsa su da harbin bindiga.

Daya daga cikin masu zanga-zangar, Ibrahim Gana, ya koka kan yadda ake sayar da kwanon shinkafa Naira 2,000 a kasuwanni, yayin da masara ta kai Naira 1,000.

INEC ta Bayyana Sakamakon Yan Majalisun Jihar Kano Guda biyu

“Ya kamata Gwamnatin Tarayya ta dauki matakin rage wahalhalun da talakawan Najeriya ke sha, mutane ba za su iya jurewa ba.”

Kakakin rundunar, DSP Wasiu Abiodun, bai amsa kiran waya don yin karin haske kan lamarin ba.

Kayan masarufi na ci gaba da yin tashin gwauron zabo a Najeriya, lamarin da ya sanya talakawa yin kira ga shugabanni su kawo musu dauki.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...

NNPPn Kano ta bayyana matsayar Kwankwaso kan batun yi wa Tinubu mataimaki a 2027

Shugabanin bangarori biyu na jam’iyyar NNPP a jihar Kano,...

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...