Tsadar Kayan Abinchi: Zanga-Zanga Ta Barke A Jihar Neja

Date:

Dandazon mutane sun mamaye Minna, Babban Birnin Jihar Neja, don nuna bacin ransu kan yadda kayan abinci ke ci gaba da tashin gwauron zabo.

Tun misalin karfe 7 na safiyar ranar Litinin, dandazon mutane suka yi tsinke suka tare hanyar Minna zuwa Bida, don nuna bacin ransu kan tsadar kayan abinci.

Hakan ya kawo tsaikon zirga-zirgar ababen hawa a birnin.

Soja ya bude wuta, ya kashe ogansa, ya raunata wasu a Sokoto

Jami’an ’yan sanda kawo dauki domin tabbatar da tsaro, amma wasu masu zanga-zangar suka yi kokarin kawo musu farmaki, lamarin da ya kai ga tarwatsa su da harbin bindiga.

Daya daga cikin masu zanga-zangar, Ibrahim Gana, ya koka kan yadda ake sayar da kwanon shinkafa Naira 2,000 a kasuwanni, yayin da masara ta kai Naira 1,000.

INEC ta Bayyana Sakamakon Yan Majalisun Jihar Kano Guda biyu

“Ya kamata Gwamnatin Tarayya ta dauki matakin rage wahalhalun da talakawan Najeriya ke sha, mutane ba za su iya jurewa ba.”

Kakakin rundunar, DSP Wasiu Abiodun, bai amsa kiran waya don yin karin haske kan lamarin ba.

Kayan masarufi na ci gaba da yin tashin gwauron zabo a Najeriya, lamarin da ya sanya talakawa yin kira ga shugabanni su kawo musu dauki.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...