Yanzu-yanzu: Kotun Ƙoli ta tabbatar da Abba Kabir a matsayin Gwamnan Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kotun koli ta yi watsi da hukuncin da kotun daukaka kara da ke Abuja ta yanke na soke nasarar Gwamna Kabir Yusuf na jihar Kano.

A ranar Juma’a ne wasu alkalai guda biyar suka tabbatar da cewa, kotun daukaka karar ta yi rashin fahimta kan soke kuri’u 165,616 na Gwamna Abba Kabir Yusuf .

Da dumi-dumi: Kotun Ƙoli ta Yanke Hukuncin Shari’ar Zaɓen Gwamnan jihar Bauchi

Alkalin kotun mai shari’a Inyang Okoro ya kuma bayyana cewa batun kasancewar Gwamna Yusuf ba dan jam’iyyar ba, wani lamari ne da ya kamata ayi shi gabanin zabe.

Wannan kotu ta ci gaba da tabbatar da cewa batun tsayar da dan takara ko daukar nauyin zabe kwata-kwata hakki ne na jam’iyya ,” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...