Kungiyar Kafafen Yada Labarai ta Intanet Ta taya Gwamna Abba Murnar Hukuncin Kotun Koli

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

 

Kungiyar kafafen yada labarai ta yanar gizo mai suna Association Online Media Guild ta taya gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf na jihar Kano murnar nasarar da ya samu a kotun koli.

A wata sanarwa da kungiyar ta raba wa manema labarai ta hannun shugabanta na riko, Abdullateef Abubakar Jos da sakataren kungiyar, Abbas Yushau Yusuf, kungiyar ta bukaci gwamnan da ya yi amfani da nasarar wajen hidimtawa al’umma.

Yanzu-yanzu: Kotun Ƙoli ta tabbatar da Abba Kabir a matsayin Gwamnan Kano

Idan dai za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito, a ranar Juma’a nan ne Kotun Koli ta mayar da Abba Kabir Yusuf a matsayin Gwamnan Jihar Kano bayan da kotun sauraren kararrakin zabe da kotun daukaka kara suka soke nasarar da ya samu a zabe.

Da dumi-dumi: Kotun Ƙoli ta Yanke Hukuncin Shari’ar Zaɓen Gwamnan jihar Bauchi

Kungiyar ‘yan jaridun ta yanar gizo ce ta tara ‘yan jaridu da suke aikin su a yanar gizo daga sassa daban-daban na kasar nan, dake da hedikwata a Kano.

Kungiyar ta bukaci gwamnan jihar da ya kyautata kyakkyawar alakar da yake da ita da ’yan jaridun yanar gizo, domin Kano ce ta biyu da ta samu dimbin kafafen yada labarai na yanar gizo baya ga jihar Lagos.

Sun bukaci Gwamnan ya kara inganta tsare-tsaren da zasu ciyar da al’ummar jihar kano gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...