Yan sanda sun karya ta labarin sace mutane a hanyar Kaduna zuwa Abuja

Date:

Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ta musanta rahoton sace matafiya a kan titin Kaduna zuwa Abuja.

“Muna son tabbatar da cewar ba sace kowa a hanyar Abuja zuwa Kaduna ba; an dai yi artabu tsakanin jami’an tsaro da ’yan bindiga a kan hanyan a ranar 6 ga watan Janairu da misalin karfe 11:30 na dare.

Al’amarin ya faru ne a lokacin da yan bindiga suka yi yunkurin tsallaka babbar hanyar da ke yankin Dogon Fili da ke kan hanyar kauyen Jere.

Talla

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, ASP Mansir Hassan ya fitar a ranar Talata.

INEC ta Sanya Ranar da Zata Gudanar da Zabukan Cike Gurbi a Kano

“Amma rundunar ’yan sanda ta fatattake su da ruwan harsasai, inda suka tsere da raunin harbin bindiga,” in ji shi.

Tinubu ya rage yawan masu yi masa rakiya yayin tafiye-tafiyensa

Hassan ya ce batun sace matafiya a kan titin babu kamshin gaskiya a cikinsa, domin kuwa babu wanda aka sace.

Sai dai ya bukaci al’ummar yankin da su zama masu sanya ido tare da kai rahoton duk wani motsi da ba su yarda da shi ba ga jami’an tsaro mafi kusa da su.

Kazalika, ya ce kwamishinan ’yan sandan jihar, Ali Dabigi, ya bukaci ’yan jarida da su rika tantance labarai da hukumomin tsaro da abin ya shafa kafin su yada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...

Mun gano yadda yan Bauchi ke mamaye dazukan Kano – Gwamnatin Kano

Daga Nazifi Dukawa     Gwamnatin jihar Kano ta ce ta gano...