Yanzu-yanzu: Kotun Ƙoli ta Yanke Hukunci kan Shari’ar zaɓen gwamnan jihar Benue

Date:

Kotun ƙoli ta yi fatali da ƙarar da aka ɗaukaka kan zaɓen gwamna Hycinth Alia na jihar Benue.

Matakin na zuwa ne bayan janye ƙarar da lauyan Mr Titus Uba na Jam’iyyar PDP, Sebastian Hon ya yi.

Titus Uba ya ƙalubalanci nasarar gwamna Hyacinth ne na jam’iyyar APC.

Talla

Sai dai kotun ƙararrakin zabe da ta ɗaukaka ƙara a Abuja sun tabbatar Alia ne halastaccen gwamnan jihar ta Benue bayan da hukumar aɓe INEC ta ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen ranar 18 ga watan Maris.

Kotun ɗaukaka ƙarar ta ce ba ta da hurumin sauraron ƙarar da aka shigar gabanta saboda batutuwan da aka yi ƙorafi a kansu sun faru ne gabanin zaɓen.

Da dumi-dumi: Kotun koli ka iya yanke hukuncin shari’ar zaɓen Kano da Legas ranar Juma’a

Kotun ta kuma ce kamata ya yi Uba ya maka mataimakin gwamna Sam Ode a babbar kotu bisa zargin mallakar takardar boge.

Ta kuma ce Uba ya gaza tabbatar da zarge-zargen da yake yi wa mataimakin gwamnan.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa yau litinin ne kotun zata yanke hukuncin karshen kan shari’ar zaɓen gwamnan jihar Benue da ta wasu jihohi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...